languageIcon
(Hausa) هَوُسَ
(Hausa) هَوُسَ
አማርኛ
العربية
Azeri
বাংলা
Bosanski
Deutsch
English
Español
Filipino
فارسي
Français
हिन्दी
Indonesia
italiano
Қазақ тілі
தமிழ்
كوردی
नेपाली
Português
Pусский
සිංහල‎
Gjuha shqipe
Kiswahili
ภาษาไทย
Türkçe
Українська
اردو
Yorùbá
中文
search
search
Wuraren da Allah Maxaukakin Sarki ya kwaxaitar da a ambace shi a cikinsu, suna da yawa

Wuraren da Allah Maxaukakin Sarki ya kwaxaitar da a ambace shi a cikinsu, suna da yawa. Ga kaxan daga cikinsu:

1/  Allah Maxaukakin Sarki ya kwaxaitar da bayinsa muminai a kan yawaita ambatonsa, da cewa: “Yak u waxanda suka yi imani! ku ambaci Allah, Ambato mai yawa. Ku kuma tsarkake shi, safiya da marece.” {Ahzab:41-42}.

2/ Allah Maxaukakin Sarki ya yi wa masu ambatonsa, maza da mata, alqawalin gafara da lada mai tarin yawa, da cewa: “Da masu ambton Allah maza, da masu ambaton Allah mata. Allah ya yi musu tanadin gafara da lada mai girma.” {Ahzab:35}.

3/ Allah Maxaukakin Sarki ya yi mana kashedi da hali irin na munafukai; suna ambatonsa Maxaukakin Sarki, amma da walákin. Allah Maxaukakin Sarki ya bayyana irin nasu ambaton da cewa: “Haqiqa, munafukai suna yaudarar Allah ne, Shi kuwa yana mayar musu da sakamakon yaudararsu. Idan suka tashi zuwa salla, sai su tahsi cikin kasala; don kawai mutane su gani. Ba su kuma ambaton Allah sai kaxan.” {Nisa’i:14}.

4/  Allah Maxaukakin Sarki ya yi mana kashedi da shagaltuwa da dukiya, da ‘yaya, tare da yin ko oho da ambaonsa Maxaukakin Sarki, ya ce: “Ya ku waxanda suka yi imani! Kada dukiyoyinku, da ‘ya’yanku su shagaltar da ku daga ambaton Allah. Duk wanda ya aikata haka, to, waxannan suna daga ciki masu hasara.” {Munafiqun:9}.    

5/  Yana da kyau kowane musulmi ya kalli muhimmanci da girman da ambaton Allah Maxaukakin Sarki yake da shi a wurinsa, hard a ya ce: “Ku ambace ni, in ambace ku.”  ya kuma ce a cikin Hadisi Qudusí: “Ina nan inda bawana yake zatona. Ina kuma tare da shi, idan ya ambace ni. idan ya ambace ni a cikin ransa, zan ambace shi a cikin raina. Idan kuma ya ambace ni a cikin wata jama’a, zan ambace shi a cikin jama’ar da ta fi wannan girma da xaukaka.”  (Buhari:7405/ Muslimu:2675), daga cikin Hadisan Abu Huraira raliyallahu anhu.

 

00:00
Simple Audio Player
- aN:aN
facebook googleplus twitter