languageIcon
search
search
brightness_1 Karanta addu’ar da aka samo a Sunna yayin shiga da fita makewayi

Sunna ne ga wanda zai shiga makewayi, ya karanta addu’ar nan, wadda ta zo a cikin ingantattun littafan hadisai guda biyu:

An samo daga Anas raliyallahu anhu, ya ce: “Manzon Allahsallallahu alaihi wa sallam ya kasance idan zai shiga makewayi yakan karanta: “Alláhumma inná aúzu bika minal- khubusi wal- khabá’isi.” (Ya Ubangiji! Ina neman tsarinka daga kowane irin sharri, da kuma miyagun halittu maza da mata.) [Buhari:6322/ Muslim:375].

Kalimar ‘khubusi’ ta Larabci tana nufin  ‘miyagun halittu maza.’ a yayin da ita kuma ta ‘khabá’isi’ take nufin ‘miyagun halittu mata.’

Idan kuma aka yi wa harafin ‘b’  xauri a cikin kalimar, aka ce: ‘khubsu’ kamar yadda take a cikin wannan Hadisi. To tana nufin kowane irin sharri. Jam’inta kuma shi ne: ‘khabá’is’ kamar na farko, amma yana nufin miyagun halittu masu mugun nufi kimshe a cikin zukata. Kenan, wannan addu’a neman tsari daga kowane irin sharri da ma’abutansa. Yin xaurin nan kuma shi ne mafi kandamewa ga ma’ana.  

- Sunna ne kuma ga wanda ya fito makewayi ya karanta:

Abin day a zo a cikin Musnada na Imamu ahmad, da Sunan na Abu Dawu, da na Tirmizi, wanda kuma albani ya inganta, daga Sayyidah A’isha raliyallahu anha, da ta ce: “Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya kasance idan ya fito daga makewayi yakan ce: “Gufrának” (Ina neman gafararka ya Ubangiji). [Ahmad:20220/ Abu Dawuda:30/ Tirmizi:7] Albani kuma ya inganta shi a cikin: Tahqíqu Mushkátul- Misábih: (1/116).

 

brightness_1 Jiran Salla

Zaunawa Masallaci a jira kamawar lokacin wata salla, Sunna ce mai girma da take bayar da lada mai yawa.

Hujja a kan wannan Sunna:

Hujja a kan wannan Sunna ita ce, Hadisin Abu Huraira raliyallahu anhu, cewa, Manzon Allah  sallallahu alaihi wa sallam ya ce: “Zaman duk da xayanku zai  jiran kamawar lokacin salla; babu abin day a hana shi komawa cikin iyalinsa sai sallar. To, kamar yana cikin sallar ne.” (Buhari:659/ Muslimu:649). Wannan jira da musulmi zai yin a kamawar lokacin salla, babu abin da ake rubuta masa sai ladar wanda yake salla.

Wata hujjar kuma ita ce, abin da aka riwaito daga Abu Huraira raliyallahu anhu, cewa, Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam ya ce: “Mala’iku suna yin salati ga duk wanda yake zaune cikin Masallaci yana jiran kamawar lokacin sallah, matuqar bai yi magana ba, suna cewa: Allah ka yi gafara gare shi, ka kuma yi masa rahama. Zaman duk da xayanku zai  jiran kamawar lokacin salla; babu abin day a hana shi komawa cikin iyalinsa sai sallar. To, kamar yana cikin sallar ne.” (Buhari:659/ Muslimu:649). Cewar da Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam ya yi: “Matuqar bai yi magana ba.”  Ba magana kawai ba, hakan na nufin matuqar bai yi wani abu da zai walwale masa arwalla ba. Hujja a kan wannan fashin baqi ita ce, wata riwayar ta Muslim da take cewa, cewa Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam ya yi:

“Matuqar bai cutar da wani a yayin zaman ba,  bai kuma yi wani abu da zai walwale masa arwalla ba,” (649). Ma’ana, sharaxin samun wannan lada shi ne, kada ya cutar da wani abokin zamansa a cikin Masallacin, kada kuma arwallarsa ta walwale.